Subhanillah Kowane Lokaci Za’a Iya Jin Labari Marar Dadi Tsakanin Adam A Zango Da Matarsa

 A kwanakinnan yan maganganu na yawo na batun A zango ya saki matar sa Safiya Chalawa sai dai ba tabbacin hakan kowa dai na dogara da akwai wata kasa kasancewar irin maganganun da Safiyan ke fadi a shafukan ta cikin shagube da kuma location dinta da ya nuna tsawon watanni tana birnin kebbi banda yan kananan gulmace gulmace da ake a ciki da wajen Masana’antar Dake Bayyana zango da matarsa basa TareSai dai a yau Adam A zangon ya warware zare da abawa kan irin matsalolin da suke samu a auren su da inda take a halin yanzu da ma matsayar auren nasa duk da yace bai sake tan ba amma ya tabbatar dan yana jarumi bazai kashe kanshi ba za’a iya jin Labari Marar Dadi a Kowane LokacinA Cikin Wani Faifan Bidiyo Adam A Zango Yayi Wani Bayani Wanda Zamu Takaita Muku Abunda Yace’ Mutane Da Yawa Na Daukarsa A Matsayin Mai Auri Saki Wadda Yayi Aure Da Yawan Gaske Kasancewar Wata Matsala Da Yake Fuskanta A Tare Da Matan Nasa Wadda Ya Zamo Family Issue Da Bai Kamata Ya Bayyana Su Ba’Inda Ya Kara Da Cewa Shima Kansa Ba’a San Ransa Ya Fito Yayi Wannan Bayani Ba Amma A Wannan Karan Ya Kamata Yace Wani Abu Akan Batun Abunda Dake Tsakaninsa Da Safeeya Chalawa Da Ake Zargin Aurensu Ya RabuInda Ya Bayyana Cewar Gaskiya Ya Samu Matsala Da Matarsa Safeeya Chalawa Tun Wasu Yan Watanni Take Gidansu.

Har Iyaye Da Yan Uwa Wayanda Ke Da Ruwa Da Tsaki Kan Auren Nasu An Zauna Amma Ba’a Samu Sasanto BaYa Bayyana Cewar Tun Lokacin Da Sukayi Aure Abubuwa Sun Faru Amma Abu Mafi Rinjaye Da Ya Hadusu Da Ita Shine Waya, Wadda Yasha Yi Mata Magana Akan Wayar Amma Bata Daina Amfani Da Ita Ba ,In Har Wayar Bata Bar Hannunta Ba To Bazasu Samu Sasanto Ba Ta Dalilin Haka Kowane Lokaci Za’a Iya Jin Labari Marar Dadi Amma Har Yanzu Ban Saketa BaYa Kara Da Cewar Tabbas Shi Ya Barta Take Sana’a A Social Media Inda Ta Bayyana Masa Cewar Ta Shiga Adashe Tana Zuba Kudi Ashe Itace Uwar Adashen Kasancewar Sirru Baza Fada Muku Abunda Ya Faru Ba Da Adashen BaHaka Zalika Ya Bayyana Cewar Babu Jituwa Tsakaninta Da Yan Uwansa Harma Da Yayansa Amma Hakan Bai Dameshi Ba Kasancewar Yawanchi Gida Ana Samun Irin Wannan MatsalarYa Bayyana Babban Abunda Ya Jawo Matsalarsu Shine Sakin Wani Bidiyo Da Tayi A TikTok Tana Rawar Bayan An Mata Lallai A Gidan Yin Lallai ,


Wadda Hakan Baimar Dadi Ba Daga Karshe Yace Mata Tace Gida Saboda Irin Matsalolin Da Yake Fuskanta A Zamantacewa Su Da ItaBayan Tace Gidansu Sai Akayi Tattauna Na Yarda Ta Dawo Gidannan Bisa Sharada Uku Na Farko Wannan Wayar Da Take Amfani Da Ita Ta Bar Hannunta Saide A Bata Karamar Wayar Da Zatana Iya Kiran Gidansu Ko Ni Da Sauran Yan UwantaNa Biyu Kuma Yace Zai Canza Mata Gida Saboda Yayansa Da Yan Uwansa Babu Jituwa Tsakaninsu Da Ita Tun Tuntuni Solution Da Ya Kamata Nayi Shine Na Canza Mata Gida, Sannan Sharadi Na Uku Shine Business Din Da Takeyi A Dakatar Da Shi Saboda Badashi Tazo Gidana Ba ,




Ni Na Yarda Tayi Kuma Yanzu Bana SoDalilin Dayasa Na Yanke Wannan Shawarar Shine Ta Bayyana Cewar Tunda Na Aureta Ita Take Daukar Dawainiyarta Sannan Tunda Ta Haifi Diyata Ko Famfas Ban Taba Saya Mata Ba Ga Gidanmu Mutane Sunkai Hamsun Aiki Kamar Zai Kasheta.


Ya Bayyana Cewar Wasu Abubuwan Da Ta Fada Sun Kazanta Wadda Muddin Al’umma Sukaji Shi Sai Sun Karyatata ,Kuma Gaskiya Magana Makusantana Yan Fim Sun Sani Yadda Nake Kula Da Mahaifiya ta.


Yayana Da MatanaInda Daga Karshe Bayan Yan Uwansa Sun Fadi Wannan Sharadi Sai Yan Uwanta Sukace’ Sun Yarda Da Zance Canza Gida ,Amma Maganar Waya Da Kuma Sana’arta Bazai Iyuba.


In Har Ba Haka Ba Saide A Hakuri Da Juna’Amma Har Ila Yau Bai Saki Matarsa Ba Kuma Baya So Ya Saketa, Kuma Baya So Masoyansa A Kullum Suna Masa Kallon Mai Auri Saki .Ta Dalilin Haka In Aka Sami Sansanto Zazu Koma Da Matarsa.


In Kuma Akasin Haka Ne To Kowane Lokaci Za’a Iya Jin Labari Marar Dadi Amma Ya Bayyana Cewar Daga Kanta Insha Allah Ya Gama Aure


Previous Post Next Post