“Ku dena haifar yaran da bazaku iya kula dasu ba” – Nafisat Abdullahi

 Fitacciyar tauraruwar fina-finan Kannywood, Nafisa Abdullahi, ta yi kira ga masu haihuwar ‘ya’ya ba tare da kula da su ba da su guji yin haka.


Ta bayyana haka ne a wasu sakonni da ta wallafa a shafinta na Tuwita ranar Asabar.


“Ku daina haihuwar ‘ya’yan da kuka san ba ku da halin kula da su,” in ji Nafisa.

“Ku daina haihuwar ‘ya’yan da kuka san ba ku da halin kula da su,” in ji Nafisa.

 

Ta kara da cewa Allah zai tuhumi mutanen da suke haifar ‘ya’ya ba tare da sauke nauyin da ya dora musu ba.

A cewarta: “Kun ga dukkan mutanen da ke haifar ‘ya’yan da ba su ji ba ba su gani ba, domin kawai su aika da su almajiranci, kuma su ci gaba da haifar karin ‘ya’ya, Allah sai ya saka wa yaran nan!!!”

 

Ta bayyana matukar bacin ranta kan yadda wasu iyaye suke tura ‘ya’yansu ‘yan shekara biyu zuwa uku almajirci.

Previous Post Next Post