Allahu Akbar Ango Ya Rasu Ana Gab Da Ɗaurin Aurensa A Jahar Katsina

 Wani matashin Ango ya rasu ana gab da ɗaura masa Aure da Amaryarsa a jihar Katsina.



Abokin karatunsa Kamilu Abubakar shi ne ya bayyana mana haka a wayar salula, inda ya bayyana cewa, motar su angon ta taso daga jihar Nasarawa zuwa jihar Katsina a lokacin ne haɗarin mota ya rutsa da su a daide marabar ƙaramar hukumar Ɗanja dake jihar Katsin, kamar yadda wakilin Katsina Post ya rawaito.

Lamarin ya faru ne saura kwana 6 a ɗaura Aurensa da Amaryarsa.

Wata majiya mai tushe daga Abokan karatunsa, Comrade Umar Musa Yar’addu’a da Mujahid Rabi’u sun bayyana cewa, sun yi waya da shi a ranar kuma sunyi chat da shi a kafar sadarwa ta Facebook, sun ce a lokacin da ya taho yayi rubutun addu’a a kafar Facebook kafin ya baro jihar Nasarawa inda yake cewa yana a hanya Allah ya kawo su gida lafiya.

Kafin rasuwar matashin, ya kammala karatunsa a Kwalejin Ilimi Ta Tarayya dake Katsina (FCE Katsina) a sashen HAUSA/ISLAMIC a 40SERIES.

Angon ɗan asalin garin Kuka-sheƙa ne dake yankin ƙaramar hukumar Malumfashi a jihar Katsina, ya rasu yana da shekaru 24 a duniya.

Previous Post Next Post